وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا
Washshamsi waduhaha
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
The Sun
وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا
Washshamsi waduhaha
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
Walqamari itha talaha
Kuma da wata idan ya bi ta.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
Wannahari itha jallaha
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا
Wallayli itha yaghshaha
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
Wassama-i wama banaha
Da sama da abin da ya gina ta.
وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا
Wal-ardi wama tahaha
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّىٰهَا
Wanafsin wama sawwaha
Da rai da abin da ya daidaita shi.
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا
Faalhamaha fujooraha wataqwaha
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
Qad aflaha man zakkaha
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
Waqad khaba man dassaha
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ
Kaththabat thamoodu bitaghwaha
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا
Ithi inbaAAatha ashqaha
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا
Faqala lahum rasoolu Allahi naqataAllahi wasuqyaha
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا
Fakaththaboohu faAAaqaroohafadamdama AAalayhim rabbuhum bithanbihim fasawwaha
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا
Wala yakhafu AAuqbaha
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).