وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallayli itha yaghsha
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
The Night
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallayli itha yaghsha
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Wannahari itha tajalla
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
Wama khalaqa aththakarawal-ontha
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
Inna saAAyakum lashatta
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ
Faamma man aAAta wattaqa
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ
Wasaddaqa bilhusna
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilyusra
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ
Waamma man bakhila wastaghna
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ
Wakaththaba bilhusna
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilAAusra
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ
Wama yughnee AAanhu maluhu ithataradda
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
Inna AAalayna lalhuda
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْـَٔاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ
Wa-inna lana lal-akhirata wal-oola
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
Faanthartukum naran talaththa
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى
La yaslaha illaal-ashqa
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Allathee kaththaba watawalla
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى
Wasayujannabuha al-atqa
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ
Allathee yu/tee malahuyatazakka
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰٓ
Wama li-ahadin AAindahu minniAAmatin tujza
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ
Illa ibtighaa wajhi rabbihial-aAAla
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
Walasawfa yarda
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).