وَٱلضُّحَىٰ
Wadduha
Inã rantsuwa da hantsi.
The Morning Hours
وَٱلضُّحَىٰ
Wadduha
Inã rantsuwa da hantsi.
وَٱلَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ
Wallayli itha saja
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
Ma waddaAAaka rabbuka wama qala
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
وَلَلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ ٱلْأُولَىٰ
Walal-akhiratu khayrun laka minaal-oola
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰٓ
Walasawfa yuAAteeka rabbuka fatarda
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَـَٔاوَىٰ
Alam yajidka yateeman faawa
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
وَوَجَدَكَ ضَآلًّا فَهَدَىٰ
Wawajadaka dallan fahada
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
وَوَجَدَكَ عَآئِلًا فَأَغْنَىٰ
Wawajadaka AAa-ilan faaghna
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
فَأَمَّا ٱلْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ
Faamma alyateema fala taqhar
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنْهَرْ
Waamma assa-ila falatanhar
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ
Waamma biniAAmati rabbika fahaddith
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).