لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
La oqsimu bihatha albalad
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
The City
لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
La oqsimu bihatha albalad
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
Waanta hillun bihatha albalad
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ
Wawalidin wama walad
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ
Laqad khalaqna al-insana feekabad
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ
Ayahsabu an lan yaqdira AAalayhi ahad
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا
Yaqoolu ahlaktu malan lubada
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ
Ayahsabu an lam yarahu ahad
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ
Alam najAAal lahu AAaynayn
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ
Walisanan washafatayn
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ
Wahadaynahu annajdayn
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ
Fala iqtahama alAAaqaba
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ
Wama adraka maalAAaqaba
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍ
Fakku raqaba
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوْ إِطْعَـٰمٌ فِى يَوْمٍ ذِى مَسْغَبَةٍ
Aw itAAamun fee yawmin theemasghaba
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ
Yateeman tha maqraba
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ
Aw miskeenan tha matraba
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ
Thumma kana mina allatheena amanoowatawasaw bissabri watawasaw bilmarhama
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
Ola-ika as-habualmaymana
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
Wallatheena kafaroo bi-ayatinahum as-habu almash-ama
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌۢ
AAalayhim narun mu/sada
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.