وَٱلْفَجْرِ
Walfajr
Inã rantsuwa da alfijiri.
The Dawn
وَٱلْفَجْرِ
Walfajr
Inã rantsuwa da alfijiri.
وَلَيَالٍ عَشْرٍ
Walayalin AAashr
Da darũruwa gõma.
وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ
WashshafAAi walwatr
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ
Wallayli itha yasr
Da dare idan yana shũɗewa.
هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِى حِجْرٍ
Hal fee thalika qasamun lithee hijr
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
Alam tara kayfa faAAala rabbuka biAAad
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ
Irama thati alAAimad
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ
Allatee lam yukhlaq mithluha fee albilad
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ
Wathamooda allatheena jaboo assakhrabilwad
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ
WafirAAawna thee al-awtad
Da Fir'auna mai turãku.
ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ
Allatheena taghaw fee albilad
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ
Faaktharoo feeha alfasad
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ
Fasabba AAalayhim rabbuka sawtaAAathab
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ
Inna rabbaka labilmirsad
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ
Faamma al-insanu itha maibtalahu rabbuhu faakramahu wanaAAAAamahu fayaqoolu rabbeeakraman
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ
Waamma itha ma ibtalahufaqadara AAalayhi rizqahu fayaqoolu rabbee ahanan
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ
Kalla bal la tukrimoonaalyateem
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
Wala tahaddoona AAala taAAamialmiskeen
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا
Wata/kuloona atturatha aklanlamma
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّا جَمًّا
Watuhibboona almala hubbanjamma
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا
Kalla itha dukkati al-ardudakkan dakka
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا
Wajaa rabbuka walmalaku saffansaffa
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ
Wajee-a yawma-ithin bijahannamayawma-ithin yatathakkaru al-insanu waannalahu aththikra
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى
Yaqoolu ya laytanee qaddamtu lihayatee
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌ
Fayawma-ithin la yuAAaththibuAAathabahu ahad
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌ
Wala yoothiqu wathaqahu ahad
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ
Ya ayyatuha annafsualmutma-inna
Yã kai rai mai natsuwa!
ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً
IrjiAAee ila rabbiki radiyatanmardiyya
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى
Fadkhulee fee AAibadee
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
وَٱدْخُلِى جَنَّتِى
Wadkhulee jannatee
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).