وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًا
WannaziAAati gharqa
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Those who drag forth
وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًا
WannaziAAati gharqa
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًا
Wannashitati nashta
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًا
Wassabihati sabha
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًا
Fassabiqati sabqa
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًا
Falmudabbirati amra
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
Yawma tarjufu arrajifa
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
TatbaAAuha arradifa
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ
Quloobun yawma-ithin wajifa
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌ
Absaruha khashiAAa
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
Yaqooloona a-inna lamardoodoona feealhafira
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًا نَّخِرَةً
A-itha kunna AAithamannakhira
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ
Qaloo tilka ithan karratun khasira
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ
Fa-innama hiya zajratun wahida
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
Fa-itha hum bissahira
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
Hal ataka hadeethu moosa
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
Ith nadahu rabbuhu bilwadialmuqaddasi tuwa
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
Ithhab ila firAAawna innahu tagha
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
Faqul hal laka ila an tazakka
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
Waahdiyaka ila rabbika fatakhsha
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
Faarahu al-ayata alkubra
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
Fakaththaba waAAasa
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
Thumma adbara yasAAa
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
Fahashara fanada
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
Faqala ana rabbukumu al-aAAla
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
Faakhathahu Allahu nakalaal-akhirati wal-oola
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰٓ
Inna fee thalika laAAibratan limanyakhsha
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا
Aantum ashaddu khalqan ami assamaobanaha
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
RafaAAa samkaha fasawwaha
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
Waaghtasha laylaha waakhraja duhaha
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
Wal-arda baAAda thalikadahaha
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
Akhraja minha maahawamarAAaha
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
Waljibala arsaha
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ
MataAAan lakum wali-anAAamikum
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
Fa-itha jaati attammatualkubra
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ
Yawma yatathakkaru al-insanu masaAAa
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
Waburrizati aljaheemu liman yara
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
Faamma man tagha
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
Waathara alhayata addunya
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Fa-inna aljaheema hiya alma/wa
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
Waama man khafa maqamarabbihi wanaha annafsa AAani alhawa
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Fa-inna aljannata hiya alma/wa
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
Yas-aloonaka AAani assaAAatiayyana mursaha
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
Feema anta min thikraha
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Ila rabbika muntahaha
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
Innama anta munthiru manyakhshaha
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
Kaannahum yawma yarawnaha lamyalbathoo illa AAashiyyatan aw duhaha
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.