عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ
AAamma yatasaaloon
A kan mẽ suke tambayar jũna?
The Tidings
عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ
AAamma yatasaaloon
A kan mẽ suke tambayar jũna?
عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ
AAani annaba-i alAAatheem
A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?
ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ
Allathee hum feehi mukhtalifoon
Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?
كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
Kalla sayaAAlamoon
A'aha! Zã su sani.
ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
Thumma kalla sayaAAlamoon
Kuma, a'aha! Zã su sani.
أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَـٰدًا
Alam najAAali al-arda mihada
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?
وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًا
Waljibala awtada
Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?
وَخَلَقْنَـٰكُمْ أَزْوَٰجًا
Wakhalaqnakum azwaja
Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?
وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا
WajaAAalna nawmakum subata
Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?
وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًا
WajaAAalna allayla libasa
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?
وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًا
WajaAAalna annaharamaAAasha
Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?
وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا
Wabanayna fawqakum sabAAan shidada
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?
وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا
WajaAAalna sirajan wahhaja
Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?
وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءً ثَجَّاجًا
Waanzalna mina almuAAsiratimaan thajjaja
Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?
لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّا وَنَبَاتًا
Linukhrija bihi habban wanabata
Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?
وَجَنَّـٰتٍ أَلْفَافًا
Wajannatin alfafa
Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?
إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَـٰتًا
Inna yawma alfasli kana meeqata
Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.
يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا
Yawma yunfakhu fee assoorifata/toona afwaja
Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.
وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًا
Wafutihati assamao fakanatabwaba
Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.
وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا
Wasuyyirati aljibalu fakanatsaraba
Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.
إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا
Inna jahannama kanat mirsada
Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.
لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابًا
Littagheena maaba
Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.
لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًا
Labitheena feeha ahqaba
Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.
لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا
La yathooqoona feehabardan wala sharaba
Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.
إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا
Illa hameeman waghassaqa
Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.
جَزَآءً وِفَاقًا
Jazaan wifaqa
Sakamako mai dãcẽwa.
إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًا
Innahum kanoo la yarjoona hisaba
Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.
وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا كِذَّابًا
Wakaththaboo bi-ayatinakiththaba
Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!
وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَـٰهُ كِتَـٰبًا
Wakulla shay-in ahsaynahu kitaba
Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.
فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا
Fathooqoo falan nazeedakum illaAAathaba
Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا
Inna lilmuttaqeena mafaza
Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.
حَدَآئِقَ وَأَعْنَـٰبًا
Hada-iqa waaAAnaba
Lambuna da inabõbi.
وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًا
WakawaAAiba atraba
Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.
وَكَأْسًا دِهَاقًا
Waka/san dihaqa
Da hinjãlan giya cikakku.
لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا كِذَّٰبًا
La yasmaAAoona feeha laghwanwala kiththaba
Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.
جَزَآءً مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًا
Jazaan min rabbika AAataan hisaba
Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.
رَّبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَـٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًا
Rabbi assamawati wal-ardiwama baynahuma arrahmani layamlikoona minhu khitaba
Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.
يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ صَفًّا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَـٰنُ وَقَالَ صَوَابًا
Yawma yaqoomu arroohu walmala-ikatusaffan la yatakallamoona illa man athinalahu arrahmanu waqala sawaba
Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.
ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا
Thalika alyawmu alhaqqu famanshaa ittakhatha ila rabbihi maaba
Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.
إِنَّآ أَنذَرْنَـٰكُمْ عَذَابًا قَرِيبًا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَـٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا
Inna antharnakum AAathabanqareeban yawma yanthuru almaro ma qaddamatyadahu wayaqoolu alkafiru ya laytanee kuntuturaba
Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"