إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Itha ashshamsu kuwwirat
Idan rãna aka shafe haskenta
The Overthrowing
إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Itha ashshamsu kuwwirat
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
Wa-itha annujoomu inkadarat
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Wa-itha aljibalu suyyirat
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Wa-itha alAAisharu AAuttilat
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Wa-itha alwuhooshu hushirat
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Wa-itha albiharu sujjirat
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Wa-itha annufoosu zuwwijat
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
Wa-itha almawoodatu su-ilat
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ
Bi-ayyi thanbin qutilat
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
Wa-itha assuhufunushirat
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
Wa-itha assamao kushitat
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Wa-itha aljaheemu suAAAAirat
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Wa-itha aljannatu ozlifat
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ
AAalimat nafsun ma ahdarat
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
Fala oqsimu bilkhunnas
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
Aljawari alkunnas
Mãsu gudu suna ɓũya.
وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Wallayli itha AAasAAas
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Wassubhi ithatanaffas
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Innahu laqawlu rasoolin kareem
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ
Thee quwwatin AAinda theealAAarshi makeen
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
MutaAAin thamma ameen
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
Wama sahibukum bimajnoon
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ
Walaqad raahu bilofuqialmubeen
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ
Wama huwa AAala alghaybi bidaneen
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍ رَّجِيمٍ
Wama huwa biqawli shaytaninrajeem
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
Faayna tathhaboon
Shin, a inã zã ku tafi?
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
In huwa illa thikrun lilAAalameen
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
Liman shaa minkum an yastaqeem
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
Wama tashaoona illa anyashaa Allahu rabbu alAAalameen
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.