سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
Saala sa-ilun biAAathabin waqiAA
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
The Ascending Stairways
سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
Saala sa-ilun biAAathabin waqiAA
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌ
Lilkafireena laysa lahu dafiAA
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ
Mina Allahi thee almaAAarij
Daga Allah Mai matãkala.
تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
TaAAruju almala-ikatu warroohuilayhi fee yawmin kana miqdaruhu khamseena alfasana
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
فَٱصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
Fasbir sabran jameela
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًا
Innahum yarawnahu baAAeeda
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
وَنَرَىٰهُ قَرِيبًا
Wanarahu qareeba
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ
Yawma takoonu assamao kalmuhl
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ
Watakoonu aljibalu kalAAihn
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
Wala yas-alu hameemun hameema
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ
Yubassaroonahum yawaddu almujrimu lawyaftadee min AAathabi yawmi-ithin bibaneeh
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ
Wasahibatihi waakheeh
Da matarsa da ɗan'uwansa.
وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ
Wafaseelatihi allatee tu/weeh
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
Waman fee al-ardi jameeAAan thummayunjeeh
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
Kalla innaha latha
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
NazzaAAatan lishshawa
Mai twãle fãtar goshi.
تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
TadAAoo man adbara watawalla
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ
WajamaAAa faawAAa
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا
Inna al-insana khuliqa halooAAa
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًا
Itha massahu ashsharrujazooAAa
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا
Wa-itha massahu alkhayru manooAAa
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ
Illa almusalleen
Sai mãsu yin salla,
ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ
Allatheena hum AAala salatihimda-imoon
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
Wallatheena fee amwalihimhaqqun maAAloom
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ
Lissa-ili walmahroom
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
Wallatheena yusaddiqoonabiyawmi addeen
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
Wallatheena hum min AAathabirabbihim mushfiqoon
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
Inna AAathaba rabbihim ghayru ma/moon
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ
Wallatheena hum lifuroojihim hafithoon
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
Illa AAala azwajihim awma malakat aymanuhum fa-innahum ghayru maloomeen
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ
Famani ibtagha waraa thalikafaola-ika humu alAAadoon
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ
Wallatheena hum li-amanatihimwaAAahdihim raAAoon
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ
Wallatheena hum bishahadatihimqa-imoon
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
Wallatheena hum AAala salatihimyuhafithoon
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍ مُّكْرَمُونَ
Ola-ika fee jannatin mukramoon
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
Famali allatheena kafarooqibalaka muhtiAAeen
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ
AAani alyameeni waAAani ashshimaliAAizeen
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
AyatmaAAu kullu imri-in minhum anyudkhala jannata naAAeem
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
Kalla inna khalaqnahummimma yaAAlamoon
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ
Fala oqsimu birabbi almashariqiwalmagharibi inna laqadiroon
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
AAala an nubaddila khayran minhum wamanahnu bimasbooqeen
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ
Fatharhum yakhoodoowayalAAaboo hatta yulaqoo yawmahumu allatheeyooAAadoon
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ
Yawma yakhrujoona mina al-ajdathi siraAAankaannahum ila nusubin yoofidoon
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ
KhashiAAatan absaruhumtarhaquhum thillatun thalika alyawmu allatheekanoo yooAAadoon
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)