ٱلْحَآقَّةُ
Alhaqqa
Kiran gaskiya!
The Reality
ٱلْحَآقَّةُ
Alhaqqa
Kiran gaskiya!
مَا ٱلْحَآقَّةُ
Ma alhaqqa
Mẽne ne kiran gaskiya?
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ
Wama adraka ma alhaqqa
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ
Kaththabat thamoodu waAAadun bilqariAAa
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ
Faamma thamoodu faohlikoo bittaghiya
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
Waamma AAadun faohlikoo bireehinsarsarin AAatiya
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَـٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
Sakhkharaha AAalayhim sabAAa layalinwathamaniyata ayyamin husooman fataraalqawma feeha sarAAa kaannahum aAAjazunakhlin khawiya
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍ
Fahal tara lahum min baqiya
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَـٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ
Wajaa firAAawnu waman qablahu walmu/tafikatubilkhati-a
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
FaAAasaw rasoola rabbihim faakhathahumakhthatan rabiya
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَـٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ
Inna lamma taghaalmao hamalnakum fee aljariya
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَآ أُذُنٌ وَٰعِيَةٌ
LinajAAalaha lakum tathkiratanwataAAiyaha othunun waAAiya
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌ وَٰحِدَةٌ
Fa-itha nufikha fee assoorinafkhatun wahida
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَٰحِدَةً
Wahumilati al-ardu waljibalufadukkata dakkatan wahida
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
Fayawma-ithin waqaAAati alwaqiAAa
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
Wanshaqqati assamaofahiya yawma-ithin wahiya
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَـٰنِيَةٌ
Walmalaku AAala arja-ihawayahmilu AAarsha rabbika fawqahum yawma-ithin thamaniya
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
Yawma-ithin tuAAradoona latakhfa minkum khafiya
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَـٰبِيَهْ
Faamma man ootiya kitabahubiyameenihi fayaqoolu haomu iqraoo kitabiyah
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَـٰقٍ حِسَابِيَهْ
Innee thanantu annee mulaqinhisabiyah
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
فَهُوَ فِى عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
Fahuwa fee AAeeshatin radiya
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
Fee jannatin AAaliya
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
Qutoofuha daniya
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ
Kuloo washraboo hanee-an bimaaslaftum fee al-ayyami alkhaliya
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَـٰبِيَهْ
Waamma man ootiya kitabahubishimalihi fayaqoolu ya laytanee lam oota kitabiyah
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
Walam adri ma hisabiyah
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
يَـٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ
Ya laytaha kanati alqadiya
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ
Ma aghna AAannee maliyah
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
هَلَكَ عَنِّى سُلْطَـٰنِيَهْ
Halaka AAannee sultaniyah
"Ĩkona ya ɓace mini!"
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
Khuthoohu faghullooh
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ
Thumma aljaheema sallooh
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَٱسْلُكُوهُ
Thumma fee silsilatin tharAAuhasabAAoona thiraAAan faslukooh
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ
Innahu kana la yu/minu billahialAAatheem
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
Wala yahuddu AAalataAAami almiskeen
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌ
Falaysa lahu alyawma hahuna hameem
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
Wala taAAamun illamin ghisleen
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ
La ya/kuluhu illa alkhati-oon
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
Fala oqsimu bima tubsiroon
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
Wama la tubsiroon
Da abin da bã ku iya gani.
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Innahu laqawlu rasoolin kareem
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
Wama huwa biqawli shaAAirinqaleelan ma tu/minoon
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
Wala biqawli kahinin qaleelanma tathakkaroon
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
Tanzeelun min rabbi alAAalameen
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ
Walaw taqawwala AAalayna baAAdaal-aqaweel
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ
Laakhathna minhu bilyameen
Dã Mun kãma shi da dãma.
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ
Thumma laqataAAna minhualwateen
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ
Fama minkum min ahadin AAanhu hajizeen
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
Wa-innahu latathkiratun lilmuttaqeen
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
Wa-inna lanaAAlamu anna minkum mukaththibeen
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ
Wa-innahu lahasratun AAala alkafireen
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ
Wa-innahu lahaqqu alyaqeen
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
Fasabbih bismi rabbika alAAatheem
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.