يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ
Ya ayyuha almuddaththir
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
The Cloaked One
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ
Ya ayyuha almuddaththir
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
قُمْ فَأَنذِرْ
Qum faanthir
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ
Warabbaka fakabbir
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ
Wathiyabaka fatahhir
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ
Warrujza fahjur
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ
Wala tamnun tastakthir
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ
Walirabbika fasbir
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ
Fa-itha nuqira fee annaqoor
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍ يَوْمٌ عَسِيرٌ
Fathalika yawma-ithin yawmunAAaseer
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍ
AAala alkafireena ghayruyaseer
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًا
Tharnee waman khalaqtu waheeda
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًا مَّمْدُودًا
WajaAAaltu lahu malan mamdooda
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
وَبَنِينَ شُهُودًا
Wabaneena shuhooda
Da ɗiyã halartattu,
وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًا
Wamahhadtu lahu tamheeda
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ
Thumma yatmaAAu an azeed
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِـَٔايَـٰتِنَا عَنِيدًا
Kalla innahu kana li-ayatinaAAaneeda
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا
Saorhiquhu saAAooda
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ
Innahu fakkara waqaddar
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Faqutila kayfa qaddar
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Thumma qutila kayfa qaddar
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
ثُمَّ نَظَرَ
Thumma nathar
Sa'an nan, ya yi tunãni
ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ
Thumma AAabasa wabasar
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ
Thumma adbara wastakbar
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
فَقَالَ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌ يُؤْثَرُ
Faqala in hatha illa sihrunyu/thar
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ
In hatha illa qawlu albashar
"Wannan maganar mutum dai ce."
سَأُصْلِيهِ سَقَرَ
Saosleehi saqar
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ
Wama adraka ma saqar
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ
La tubqee wala tathar
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
لَوَّاحَةٌ لِّلْبَشَرِ
Lawwahatun lilbashar
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ
AAalayha tisAAata AAashar
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةً ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةً لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَـٰنًا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌ وَٱلْكَـٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَـٰذَا مَثَلًا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ
Wama jaAAalna as-habaannari illa mala-ikatan wamajaAAalna AAiddatahum illa fitnatan lillatheenakafaroo liyastayqina allatheena ootoo alkitabawayazdada allatheena amanoo eemananwala yartaba allatheena ootoo alkitabawalmu/minoona waliyaqoola allatheena feequloobihim maradun walkafiroona mathaarada Allahu bihatha mathalan kathalikayudillu Allahu man yashao wayahdee man yashaowama yaAAlamu junooda rabbika illa huwa wamahiya illa thikra lilbashar
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
كَلَّا وَٱلْقَمَرِ
Kalla walqamar
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ
Wallayli ith adbar
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ
Wassubhi ithaasfar
Da sãfiya idan ta wãye.
إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ
Innaha la-ihda alkubar
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
نَذِيرًا لِّلْبَشَرِ
Natheeran lilbashar
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ
Liman shaa minkum an yataqaddama awyataakhkhar
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ
Kullu nafsin bima kasabat raheena
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
إِلَّآ أَصْحَـٰبَ ٱلْيَمِينِ
Illa as-haba alyameen
Fãce mutãnen dãma.
فِى جَنَّـٰتٍ يَتَسَآءَلُونَ
Fee jannatin yatasaaloon
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ
AAani almujrimeen
Game da mãsu laifi.
مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ
Ma salakakum fee saqar
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ
Qaloo lam naku mina almusalleen
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ
Walam naku nutAAimu almiskeen
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ
Wakunna nakhoodu maAAa alkha-ideen
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
Wakunna nukaththibu biyawmi addeen
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ
Hatta atanaalyaqeen
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ
Fama tanfaAAuhum shafaAAatu ashshafiAAeen
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ
Fama lahum AAani attathkiratimuAArideen
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌ مُّسْتَنفِرَةٌ
Kaannahum humurun mustanfira
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ
Farrat min qaswara
Sun gudu daga zãki.
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًا مُّنَشَّرَةً
Bal yureedu kullu imri-in minhum an yu/tasuhufan munashshara
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ
Kalla bal la yakhafoonaal-akhira
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌ
Kalla innahu tathkira
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
Faman shaa thakarah
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ
Wama yathkuroona illaan yashaa Allahu huwa ahlu attaqwawaahlu almaghfirat
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.