إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
Itha assamao inshaqqat
Idan sama ta kẽce,
The Sundering
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
Itha assamao inshaqqat
Idan sama ta kẽce,
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ
Wa-itha al-ardu muddat
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
Waalqat ma feeha watakhallat
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَـٰقِيهِ
Ya ayyuha al-insanuinnaka kadihun ila rabbika kadhanfamulaqeeh
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ
Faama man ootiya kitabahubiyameenih
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
Fasawfa yuhasabu hisabanyaseera
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
Wayanqalibu ila ahlihi masroora
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ
Waamma man ootiya kitabahu waraathahrih
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًا
Fasawfa yadAAoo thuboora
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
Wayasla saAAeera
Kuma ya shiga sa'ĩr.
إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
Innahu kana fee ahlihi masroora
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
Innahu thanna an lan yahoor
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًا
Bala inna rabbahu kana bihi baseera
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ
Fala oqsimu bishshafaq
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
Wallayli wama wasaq
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ
Walqamari itha ittasaq
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
Latarkabunna tabaqan AAan tabaq
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
Fama lahum la yu/minoon
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
Wa-itha quri-a AAalayhimu alqur-anula yasjudoon
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ
Bali allatheena kafaroo yukaththiboon
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
Wallahu aAAlamu bimayooAAoon
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
Fabashshirhum biAAathabin aleem
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ
Illa allatheena amanoowaAAamiloo assalihati lahum ajrun ghayrumamnoon
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.